1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ƙasar Libiya na fama da ƙaranci abinci

July 5, 2011

Duban jama'a na fuskantar barazanar' yunwa saboda rashin abinci a sassan daban daban na ƙasar a sakamakon yaƙin da ake yi

Kanal Muammar GaddafiHoto: dapd

Hukumar samar da abinci ta Majalisar Dinkin Duniya wato PAM ta ce gomai na duban jama'a a ƙasar Libiya na fama da ƙaranci cimakka,Hukumar wacce wasu wakilan ta suka kammala wata ziyara a lordinan Nalout da Wazin da Jadu da kuma Zintan dake a yankin yammaci ta ce jama'ar suna cikin wani mawuyacin hali na matsi inda shaguna da kantuna suke a kule,sannan kuma ma'aikatan gwamnati ba a biyashesu ba kuɗaɗen albashi ba tun cikin watan feberu da ya gabata.

Itama ƙungiyar Red Cross ta baiyana fargaban ta akan rashin kayayyakin aiki da magungunan a cikin asibitoci inda kuma ake fama da ƙarancin mai'aikata.A halin da ake ciki kuma wani harin da dakarun kanal Muammar Gaddafin suka kai a garin Misrata ya yi sanadiyyar mutuwar mutane goma sha ɗaya

Mawallafi: Abdourahamane Hassane
Edita : Zainab Mohammed Abubakar