Hukumar Yaki da Cin-hanci da Rashawa ta Najeriya wato EFCC, ta zargi matasa da rashin kai korafin ayyukan zamba da ake tafkawa. Sai dai matasan na zargin hukumar ta EFCC da rashin hobbasa yadda ya kamata, wajen kama 'yan siyasa da ake zargi da cin-hanci da rashawa a kasar.