1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ƙoƙarin sasanta rikicin ƙasar Kongo

Ibrahim SaniDecember 27, 2007

An ɗage taron sulhu da aka shirya gudanarwa, a tsakanin Gwamnatin Kongo da wakilan ´yan tawaye. Ma´aikatar cikin gida ta ƙasar ta ce za a gudanar da taron ne, a ranar 6 ga watan Janairun sabuwar shekara. Taron zai mayar da hankali ne wajen kawo ƙarshen rikicin dake wanzuwa ne a gabashin ƙasar.Ci gaba da faruwar tashe-tashen hankula a gabashin ƙasar, a yanzu haka ya haifar da hijirar ɗaruruwan mazauna wannan yanki. Ana sa ran wannan taro na gaba, zai samu halartar shugaban ƙungiyyar ´yan tawayen Janar Laurent Nkunda.