ƙungiyar Mend ta bayyana kashe sojoji 9 na gwamnatin Nigeria
March 9, 2006A Tarayya Nigeria, matasa masu nema yancin yankin Niger Delta, sun bayyana kashe sojoji 9 na gwamnati, a sakamakon wata arangama da su ka yi.
Kakakin ƙungiyar Mend ya ce, sun hallaka wannan sojoji a cikin wata taho mu gama, ta tsawon mintina 45,da su ka yi, kussa da yankin Okerenkoko, bayan da a cewar sa, tawagar sojojin ta farma dakarun su.
Ya ce kuma wannan saban hari , ya kara harzuka aniyar su, ta ƙwatar yancin Niger Delta, mai arzikin man petur.
Idan dai ba a manta ba, har yanzu ƙungiyar Mend, na tsare da jami´ai 3, na ƙasashen ƙetare da su ka haɗa da ɗaya na Britania,da 2 Amurikawa.
A ɗaya wajen kuma, rahotani sun bayana cewa gwammnatin tarayya ta hidda Jannar Elias Zamani shugaban rundunar gwammnati a yankin Niger Delta, bayan an tuhume shi, da hannu cikin satar man petur.