Najeriya: Jam'iyyar PDP ta zabi sabbin shugabanninta
November 14, 2025
Duk da kasancewa mafi dadewa a cikin fagen siyasar tarayyar Najeriya, 'yan sao'i da ke tafe dai na da tasirin gaske bisa makomar jam'iyyar PDP ta adawa.
Wata sanarwar PDP dai ta sa kafa ta shure barazana ta kotuna, da ma adawar wani bangare cikin gidan jam'iyyar, tare da yanke hukuncin fara babban taron.
To sai dai kuma rabuwar na kara bayyana in da rasan PDP a mafi yawa na kudanci na kasar ke shirin su kauracewa taron.
Can ma a arewa dai PDP na kallon tawaye daga jihohi irin na su Sokoto da Jigawa da ya'yansu ke fadin ba su shirin taka rawa cikin babban taron da za'a fara a garin Ibadan.
Tun farko wata kotu a Abuja ta amince da bukatar tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido na dakatar da babban taron duk da kasancewar mafi yawa na ya'yan jam'iyyar sun isa birnin na Ibadan.
Ruhi da kila ma makomar PDP bayan taron Ibadan din da,i daga dukka na alamu na shirin ta'allaka bisa arewacin kasar da ke da gwamnonin jam'iyyar har guda Bakwai.