1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shigar da mata cikin harkokin gudanarwa a arewacin Najeriya

Binta Aliyu Zurmi MNA
November 12, 2018

Duba da yadda ake samun koma baya wajen shigar mata cikin harkokin gudanarwa a kasashe masu tasowa, a shekarar 2000 Majalisar Dinkin Duniya ta samar da kudiri domin baiwa mata dama a dukkan matakai.

Yachilla Bukar von "Dandal Kura"
Hoto: DW/T.Mösch

Batun sanya mata cikin harkokin gudanarwa da samar da zaman lafiya batu ne da ba safai wasu kasashe masu tasowa ke baiwa kulawar da ta dace ba. Wannan shi ya sanya Majalisar Dinkin Duniya karkashin shirinta mai "Lura da Mata na Duniya" wato UN-Women ta bullo da wani shiri na musamman a jihohi uku a arewacin Najeriya wanda aka yi wa taken “Tallafawa harkokin sanya Mata samar da zaman lafiya a arewacin Najeriya.

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani