SiyasaAfirka
Najeriya ta fitar da sunayen 'yan wasanta na gasar AFCON
December 26, 2021Talla
Hukumar Kwallon Kafar Najeriya, NFF ta sanya dan wasa Victor Osimhen, dan kasar da ke buga wa kungiyar Napoli ta Italiya a cikin 'yan wasan da za su kare mata mutunci a fafatawar da za a yi da ita a gasar kwallon kafar Afirka ta AFCON.
Victor Osimhen na cikin hutunsa na watanni uku a Napoli ne bayan wani rauni da ya samu a watan Nuwamba a fuskarsa. Amma tun a farkon makon nan aka gan shi yana atisaye, sannan ya wallafa cewa yana fatar zai shiga cikin 'yan wasan da za su buga wa Najeriya a gasar ta AFCON wace ake sa ran gudanarwa a watan gobe na Janairu a kasar Kamaru.