AFCON: Masar ta tsaurara matakan tsaro
June 21, 2019![Cairo International Stadium](https://static.dw.com/image/49264470_800.webp)
Talla
Mukaddashin shugaban hukumar kula da wasan kwallon kafar Masar Ahmed Shoubier ne ya tabbatar da hakan inda ya kara da cewar za a yi amfani ne da jiragen ne a dukannin filayen wasanni don tabbatar da tsaro yayin gasar.
Wannan dai shi ne karo farko da za a dauki irin wannan matakin a gasar ta cin kofin na kasashen Afirka. Nan gaba kadan ne kuma za a fara gasar inda za a yi wasan farko inda mai masaukin baki wato Masar za ta taka leda kasar Zimbabuwe.