AFCON: Masar ta tsaurara matakan tsaro
June 21, 2019
Talla
Mukaddashin shugaban hukumar kula da wasan kwallon kafar Masar Ahmed Shoubier ne ya tabbatar da hakan inda ya kara da cewar za a yi amfani ne da jiragen ne a dukannin filayen wasanni don tabbatar da tsaro yayin gasar.
Wannan dai shi ne karo farko da za a dauki irin wannan matakin a gasar ta cin kofin na kasashen Afirka. Nan gaba kadan ne kuma za a fara gasar inda za a yi wasan farko inda mai masaukin baki wato Masar za ta taka leda kasar Zimbabuwe.