1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutum 15 sun mutu a yunkurin neman visa

Ramatu Garba Baba
October 21, 2020

Mutum kimanin 15 ne suka mutu a yayin wani cunkoson jama'ar da ke kokarin neman takardar visa don samun izinin shiga kasar Pakistan da ke makwabtaka da kasar ta Afghanistan.

Afghanistan Toten nach einem Explosion in Provinz Wardak
Hoto: Ashaq Akrami/DW

Yan kasar Afghanistan kimanin goma sha biyar ne suka rasa rayukansu a sanadiyar cunkoson da aka samu a kusa da ofishin jakadancin kasar Pakistan da ke kasar, goma daga cikin mamatan mata ne sauran kuma tsofaffi.

Rahotanni sun ce, lamarin ya auku ne a yayin da mutum sama da dubu uku, ke rige-rigen bin layi don samun takardar visar shiga kasar Pakistan. Kawo yanzu dai babu karin haske daga jami'an ofishin jakadancin na Pakistan a game da lamarin.