1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Akalla mutum 12 sun halaka a Peru

December 2, 2025

Baya ga wadanda suka rasu akwai wasu 20 da suka jikkata sakamakon zaftarewar kasar.

Akwai malamai da likitoci a cikin wadanda suka mutu.
Akwai malamai da likitoci a cikin wadanda suka mutu.Hoto: COER/AFP

Akalla mutum 12 sun mutu a yayin da wasu 20 kuma sun jikkata a Peru bayan zaftarewar kasa ta nutsar da wasu jiragen ruwa biyu a kogin Ucayali, a yankin Amazon na kasar, ranar Litinin.

Hukumar lafiya a yankin ta ce har yanzu ana neman mutane biyu da suka bace, bayan faruwar lamarin da misalin ƙarfe 4:20 na safe a gogon yankin (0900 GMT) a tashar jiragen ruwa ta Iparia.

Mutum 18 sun mutu a hadarin mota a Peru

Jiragen ruwan biyu na kan hanyar zuwa wasu yankuna ne a bakin kogin da zaftarewar kasar ta auku ranar Litinin.

Tashar yada labarai ta gwamnati, mai suna Andina, ta ruwaito cewa rundunar ‘yan sanda da sojojin ruwa sun tura jami’ai ta jiragen sama domin aikin ceto.

Zaben shugaban Peru zagaye na biyu

Hukumomi suka ce daga cikin fasinjojin jirgin akwai malaman makaranta da kuma likitoci wadanda suka rasa rayukansu.