1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Al-Burhan ya tsallaka rijiya da baya

Usman Shehu Usman
July 31, 2024

Wani harin jirgi marar matuki ya fada a tsakiyar filin biki da shugaban gwamnatin sojin Sudan Janar Abdel Fattah al-Burhan ke halarta tare da halaka wasu mutane .

Darfur Zerstörung Lebensmittelmarkt
Hoto: AFP

Janaral Abdel Fattah al-Burhan babban hafsan sojan Sudan wanda sojojinsa ke gobza yaki da rundunar RSF, cikin gaggawa aka zakuloshi a wani sansanin sojan kasar da ya kai wa ziyara, inda aka kai harin da jirgi marasa matuki a daidai lokacin da yake ziyara cikin sansanin sojan. Hukumomi suka ce akalla mutane biyar suka mutu yayin wani da harin ya fada tsakiyar wani biki da aka shirya gudnarwa a barikin sojan kasar mai nisan kilo mita 100 daga Port Sudan, inda yanzu haka gwamnatin da sojojin Sudan ke jagoranta take da zama. Kafin harin an dai ga shugaba Burhan yana jawabin kai tsaye a gidan talabijin din kasar kafin a katse shirin ba zato. kazancewar yaki ya tilastawa gwamnatin soja kaura daga Khartoum babban birnin kasar izuwa Port Sudan. A yanzu haka mayakan RSF sune ke iko da akasarin birnin na Khartoum da wasu manyan jihohi kamarsu Kordofan da jihar Aljazira ta Tsakiya da kuma Arewacin Darfuh.