1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

al-Shabab sun kashe mutane 12 a Kenya

October 25, 2016

A kalla mutane 12 ne suka mutu a wani harin bam da ake zargin 'yan ta'addan Somaliya suka kaddamar a garin Mandera da ke arewa maso gabashin kasar Kenya.

Kenia Al Shabab Terroranschlag
Hoto: picture-alliance/dpa

'Yan sanda da ke yankin Mandera a kan iyaka da kasar Somaliya sun tabbatar da aukuwar harin sun ce suna zargin mayakan kungiyar al-Shabab na kasar Somaliya ne da kaddamar da harin da ya yi sanadiyar rayukan fararen hula. Hukumomin 'yan sandasun ce maharan sun zo da manyan makamai sannan suka tashi bam a wani gidan saukan baki na Bishoro inda kusocin gwamnati ke sauka.

Babu dai martani daga kungiyar ta al-Shabab da ake zargi da kai wannan hari, to amma kungiyar ta sha alwashin ci gaba da kai kai hare-hare mai kama da ramuwar gayya da daukar fansa a kasar kenya tun bayan da gwamnatin Kenya ta jibge jami'an tsaronta a Somaliya da nufin murkushe ayyukan ta'addanci kungiyar al-Shabab.