1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mayakan al-Shabab sun kashe sojojin Kenya

Abdul-raheem Hassan
July 29, 2026

Mayakan sun halaka akalla jami’an tsaron gwamnati guda biyar a wata arangama a gundumar Mandera, kusa da kan iyaka da kasar Somaliya.

Mayakan al-Shabaab na atisaye da makamai a wajen birnin Mogadishu
Mayakan al-Shabaab na atisaye da makamai a wajen birnin MogadishuHoto: picture alliance / AP Photo

‘Yan sanda sun na ci gaba da bin diddigin maharan, bayan da wata tawagar karin jami’ai da aka tura yankin ta gamu da wani bam da aka binne a hanya, wanda ya lalata wata motar sulke. Sai dai ba a samu asarar rai ba.

A watan Janairu, ‘yan sanda sun ce mayakan sun kashe wani shugaban kauye da kuma wani malami a gundumar Garissa da ke makwabtaka da yankin.

Hare-haren al-Shabab a yankin na yawan kai wa sojoji da fararen hula hari don cimma burin kifar da gwamnatin Somalia, tare da kafa nata mulki bisa tsauraran dokokin shari’ar Musulunci.