1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaSiriya

Ahmed al-Sharaa zai je Majalisar Dinkin Duniya

Lateefa Mustapha Ja'afar
August 25, 2025

Shugaban kasar Siriya na ruko Ahmed al-Sharaa zai yi jawabi a taron Babban Zauren Majalisar Dinkin Duniya, wanda za a yi a birnin New York na Amurka a watan Satumbar da ke tafe.

Siriya | Shugaban Kasa | Ahmed al-Sharaa | Jawabi | Majalisar Dinkin Duniya
Shugaban gwamnatin rikon kwaryar Siriya Ahmed al-SharaaHoto: Izettin Kasim/Anadolu/picture alliance

Ahmed al-Sharaa wanda ya kwace iko a hannun gwamnatin hambararren shugaban kama-karya Bashar al-Assad a watan Disambar bara, zai kasance shugaban kasar Siriya na farko da zai yi jawabi ga Babban Zauren Majalisar Dinkin Duniyar. Wani jami'in ma'aikatar harkokin wajen Siriyan da ya nemi a sakaye sunansa saboda ba shi da izinin yin magana da 'yan jarida ne, ya tabbatar da hakan ga kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP.