1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Bala'iMozambik

Mozambik cikin tasku sanadin ambaliya

Lateefa Mustapha Ja'afar
January 20, 2026

Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa, mummunan ibtila'in ambaliyar ruwa da ya afkawa Mozambik ya kara ta'azzara yanayin daukin gaggawa da ake bukata a kasar.

Mosambik | Boane | 2026 | Ambaliyar Ruwa
Ambaliyar ruwa ta jefa al'umma cikin halin ni 'yasu a MozambikHoto: Amilton Neves/REUTERS

Shugabar Ofishin Hukumar Bayar da Agajin Jin-kai ta Majalisar Dinkin Duniya OCHA a Mozambik Paola Emerson ta bayyana cewa, a yanzu kimanin sama da mutane rabin miliyan ne ke neman daukin gaggawa a kasar. Mamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya a Mozambik da kuma makwabciyar kasa Afirka ta Kudu da aka kwashe tsawon makonni a tsugawa, ya halaka kimanin mutane 150 kamar yadda mahukuntan kasashen biyu suka tabbatar.