Amincewa da dokar haramta takara a Masar
April 24, 2012![epa03157246 Egyptian parliament speaker Saad al-Katatni (R) casts his vote during elections to choose members of constituent assembly tasked with drafting the new constitution, in Cairo, Egypt, 24 March 2012. Media reports stated that a joint parliament session convened on 24 March to elect the 100-member committee that will draft Egypt's post-revolution constitution. The committee will be made up of 50 members from the parliament, while the remaining 50 will be legal experts, academics, intellectuals, unions' members and religious scholars. EPA/STRINGER +++(c) dpa - Bildfunk+++](https://static.dw.com/image/15834158_800.webp)
Hukumomin mulkin soja na Masar sun rattaɓa hannu kan dokar da ke haramta ma waɗanda aka damawa da su a lokacin mulkin Hosni Mubarak tsayawa takara a zaɓen shugaban ƙasa. Wannan dokar ta shafi waɗanda suka taɓa riƙe muƙamin shugaban ƙasa, ko mataimakin shugaba, ko ma dai firaminista, shekaru 10 kafin awan gaba da guguwar neman sauyi ta yi da kujerar mulkin Mubarak. Kana wannan doka ta haramta wa mambabin kwamitin ƙoli na jam'iyar da ta shafe shekaru ta na riƙe mulkin Masar tsayawa takara. Ɗaya daga cikin waɗanda wannan mataki zai yi tasiri kansa, shi tsohon firaminista Ahmed Chafiq.
A ranakun 23 da kuma 24 ne za a gudanar da zagayen farko na zaɓen shugaban ƙasa a Masar. Sai dai kuma har yanzu majalisar sojoji da ke tafiyar da mulki ba ta samar wa ƙasar da sabon kundin tsarin mulki kamar yadda ta alkawarta ba. Lamarin da ke haddasa shakku tsakanin ɓangarori na ƙasar game da aniyarsu ta wanke hannaye daga madafun iko a watan yuli mai zuwa idan Allah ya yarda.
Mawallafi: Mouhamadaou Awal
Edita: Umaru Aliyu