1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin kasuwancin Amirka da China

Yusuf Bala Nayaya
December 19, 2018

China da Amirka sun sake musayar kalamai a hukumar kasuwanci ta duniya WTO a inda jakadan Amirka ya zargi China da satar fasaha yayin da jakadan China shi ma ya nuna yatsa ga Amirka a matsayin mai aikata wannan ta'asa.

Symbolbild USA-China-Handelskrieg
Hoto: Colourbox

Wannan cece-kuce na zuwa ne yayin da kasashe suka jeru suna suka ko ma kalubalantar tsare-tsaren gwamnatin Shugaba Donald Trump na Amirka kan harkokin na kasuwanci yayin taron sake nazartar harkokin na kasuwancin duniya da ake yi daga lokaci zuwa lokaci karkashin hukumar ta WTO. A wannan rana ta Laraba ce dai ke zama rana ta biyu da ake zama na sirri kan kasar ta Amirka bayan zaman da aka yi a ranar Litinin.

Jakadan na Amirka dai Dennis Shea ya bukaci a mayar da hankali kan kasar ta China wacce ya ce akwai bukatar ta takure harkoki na masana'antunta kasancewar tana samar da kayayyaki marasa inganci da take jibgewa a kasashen ketare.