1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amirka ta sake magana kan sojojinta da ke Siriya

January 6, 2019

Amirka ta ce janye dakarunta daga Siriya, zai dogara ne da nasarar kakkabe mayakan IS da kuma tabbaci kan makomar Kurdawa.

USA John Bolton
Hoto: picture alliance/AP Photo/C. Owen

Hukumomin Amirka sun ce batun janye dakarun kasar daga Siriya, zai dogara ne da nasarar kakkabe mayakan IS da ma samun tabbaci daga Turkiyya kan makomar mayakan Kurdawa.

Mashawarcin Shugaba Donald Trump kan harkokin tsaro, John Bolton, wanda ya bayyana hakan a ranar Lahadi, ya ce magana ta gaskiya babu jadawali kan janyewar dakarun na Amirka a dai halin da ake ciki.

Jami'in ya fadi hakan ne a wata ziyararsa a Isra'ila, lokacin da yake tabbatar wa babbar kawar Amirkar wannan batu.

Cikin watan Disambar da ta gabata ne dai, Shugaba Trump, ya sanar da shirin janye sojoji 2000 a yankin arewa maso gabashin Siriyar, saboda abin ya ce na karya lagon kungiyar IS da aka yi.

Sai dai fa bai sami amincewar manyan kasashen yamma ba.