1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Donald Trump ya ce za su kori bakin haure

Abdourahamane Hassane
June 18, 2019

Amirka za ta soma korar bakin haure daga makon gobe wadanda ke zaune a kasar ba su da takardun izinin zama.

USA Weißes Haus Washington | Donald Trump, Präsident mit angeblichem Mexiko-Abkommen
Hoto: Getty Images/AFP/J. Watson

Shugaba Donald Trump wanda ya bayyana haka a shafinsa na Twitter ya ce akwai miliyoyin mutane da ke zaune a Amirka wadanda suka shiga kasar ba cikin kai'da ba, wadanda ya ce  za su mayar da su kasashensu da gaggawa daga duk inda suka zo. Tun farko Amirka ta gargadi kasashen Amirka ta tsakiya da cewar za tai daina ba su tallafin kudade inda har ba su dau matakan dakatar da tudadar 'yan gudun hijira ba.