Amirka za ta tura kwararrun sojoji Najeriya
February 27, 2016Talla
Idan Amirka ta aiwatar da wannan shawara, to hakan zai yi nuni da irin ci gaban da ake samu a huldar dipolomasiyya tsakaninta da Najeriya, inda a shekara ta 2014 dangantakar ta yi tsami tsakaninsu.
Gwamnatin da ta shude ta Goodluck Jonathan a baya ta nuna rashin jin dadinta ga matakin da kasar ta Amirka ta dauka na kin sayar wa Najeriyar makamai, bisa zarginta da take hakkokin bil-Adama musamman daga sojojinta, inda aka watse baram-baram bisa matakin horas da sojojin na Najeriya.
A watan Yuli dai da ya gabata ne Shugaba Muhammadu Buhari ya samu kyaukkyawan tarbo daga hukumomin kasar ta Amirka.