Hakkin dan AdamHabasha
Amnesty ta zargi sojoji da yi wa mata fyade a Habasha
September 5, 2023![](https://static.dw.com/image/66168546_800.webp)
Talla
Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International ta ce sojojin kasar Iritiriya bisa hadin gwiwa da dakarun gwamnatin Habasha sun aikata munanan laifukan cin zarafin Bil Adama a yankin Tigray na Habasha.
Amnesty ta ce duk da tsagaita wuta da aka yi a yankin, sojojin Iritiriya na halaka fararen hula tare da yi wa mata fyade - karfi da yaji. Rahoto na musamman da kungiyar ta fitar a ranar Litinin ya ce dakarun Iritiriya na kuma kwasar wa jama'an yankin Tigray dukiya a matsayin ganima. Amnesty ta ce wadannan laifuka ne masu muni da aka aikata bayan sanya hannu a kan yarjejeniyar samar da zaman lafiya a yankin.