Amurka da Rasha na gasa tsakaninsu don yin tasiri a Sahel
February 5, 2026
Ministan harkokin wajen Mali Abdoulaye Diop, ya karbi bakuncin wani babban jami'in Amurka domin tsara "sabon zubi" na dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu. Nick Checker, wanda ke jagorantar harkokin Afirka a ma'aikatar harkokin wajen Amurka, ya yi amfani da wannan dama wajen girmama 'yancin cin gashin kan Mali.
Dama kafin ziyararsa, Checker ya wallafa a shafinsa na X cewa Amurka na son "tattaunawa da sauran gwamnatoci a yankin Sahel ciki har da Burkina Faso da Nijar kan harkokin tsaro da tattalin arziki da aka raba."
Amurka na magance kura-kuran da ta tafka a baya
"A bayyane yake cewa Amurkawa ba su damu da dimukuradiyya a yankin Sahel a yanzu ba," in ji Ulf Laessing, darektan gidauniyar Konrad Adenauer a yankin sahel, inda ya ce: "Sun dauki matakin da ya dace da zamani. Wannan na nufin cewar jami'an Amurka na son gyara "kuskuren manufofinsu na baya."
Mali, Nijar da Burkina Faso sun katse ko kuma sun rage dangantaka da Faransa da ta yi musu mulkin mallaka da sauran abokan hulda na yammancin duniya, inda suka rungumi kasar Rasha. Sannan sun raba gari da makwabtansu na kasashen kungiyar ECOWAS ta yammacin Afirka tare da kafa kungiyarsu ta yankin Sahel (AES).
"Ya kamata mu yi maraba da damar da Amurka ta bai wa kasashen AES da Faransa da EU ke son mayarwa saniyar ware, don tattaunawa," in ji Dr. Gnaka Lagoke, malami a fannin tarihi a Jami'ar Lincoln da ke Pennsylvania.
Taimakon Rasha wajen dakile hare-hare a Nijar da Mali
Mali ta fada cikin matsalar tsaro tsaro tun daga shekarar 2012, inda sojojinta ke fafatawa da kungiyoyin 'yan ta'adda ISWAP da na JNIM mai alaka da Al-Qaeda. Gwamnati ta yi alkawarin dakile ta'addanci, amma hare-haren na ci gaba da wakana. Sannan a baya bayan nan, an kai hari a filin jirgin sama na birnin Nijar, Niamey, wanda ISWAP ta dauki alhakinsa.
Amma ziyarar Checker ta zo ne a daidai lokacin da Rasha ke fadada tasirinta a yankin Sahel, ciki har da aika sojoji na haya na rundunar Africa Corps.
"Rundunar sojojin Afirca Corps ta ma'aikatar tsaron Rasha da Sojojin Nijar sun hada gwiwa wajen dakile harin, inda suka kashe 'yan ta'adda kusan 20 tare da kwace makamansu" in ji ma'aikatar harkokin wajen Rasha a cikin wata sanarwa.
Rundunar ta Rasha "za ta ci gaba da bayar da gudummawa mai kyau wajen karfafa tsaron yankin, tare da taimakawa da nufin kara karfin shirin yaki na sojoji ta hanyar horar da jami'an tsaro," in ji sanarwar.
Kungiyar JNIM ta kai wani hari kwanan nan a Mali, inda majiyoyi suka shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa akalla direbobi 15 ne suka mutu a wani hari da aka kai kan ayarin tankokin mai.