Ansa tambayoyi a majalisar gari
October 16, 2020![USA Townhalls Fragestunde Trump Biden](https://static.dw.com/image/55292561_800.webp)
Talla
Dukkanin 'yan takarar biyu sun assasa hujjojinsu da suke ganin ya kamata a zabe su.
Batun annobar coronavirus shi ne ya fi mammaye taron, da aka tambayi Mr Trump a kan batun saka takunkumi kasancewar a baya an sha kai ruwa rana da shi game da batun, Mr Trump ya ce yana nan a kan bakar shi, duk da cewar yana goyon bayan sanya makarin, ya kuma kara da cewar kaso 85 cikin dari na wadanda suka kamu da cutar masu saka takunkumin ne.
A nashi bangaren madugun adawa Biden ya yi amfani da wannan dama wajen caccakar shugaban na Amurka a kan yadda ya ke wa lamarin cutar rikon sakainar kashi.