Amurka ta fice daga yarjejeniyar kula da 'yan gudun hijira
December 3, 2017Talla
Yarjejeniyar kasa ta kasa da aka cimma a watan Satumban 2016, na da nufin karfafa yadda za'a kula da lamuran 'yan gudun hijirar a duniya baki daya, kamar yadda hukumar kula da 'yan gudun hijirar ta MDD ta nunar.
Kazalika yarjejeniyar na da nufin samar da shiri na bai daya, ta yadda kasashe za su tabbatar da kare martabar 'yan gudun hijirar da duk wani nau'i na tozartawa da nuna wariya daga al'umma.
Sai dai a cewar jakadar Amurka Haley, tanadin yarjejeniyar wanda kasashen da suka rattaba hannu ke shirin fara aiwatarwa a shekara ta 2018 mai kamawa, bai dace da akidojin Amurka ba.