1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaArewacin Amurka

Amurka ta haramta ba da biza ga Nijar da wasu kasashe

December 17, 2025

Amurka ta sanar da fadada haramcin ba da takardun izinin shiga kasar zuwa kasashe 39 ciki har da yankin Falasdinu da Siriya da kuma wasu kasashen Afirka.

USA Antrag für ein Visum/Symbolbild
Hoto: Olga Yastremska/Pond5 Images/IMAGO

Jamhuriyyar Nijar da Mali da Burkina Faso da kuma Sudan ta Kudu na daga cikin kasashen da Trump ya haramta wa al'ummarsu shiga kasar ta Amurka kama daga'yan yawon bude ido da dalibai da kuma 'yan kasuwa.

Katin bayani: Amurka ta soke bizar wasu 'yan kasashen ketare

Kafin daukar wannan matakin, Shugaba Trump ya sanya hannu kan kudurin haramta wa 'yan kasashen Afghanistan da Myanmar da Chadi da Jamhuriyyar Dimukuradiyyar Kwango da Equatorial Guinea da Eritrea da Haiti har ma da Iran da Libya da Somaliya da Sudan da kuma Yemen shiga kasar tun a watan Yunin 2025.

Hukumomin Washington DC sun sanar da cewa haramcin bada bizar zai fara aiki ne daga ranar 1 ga watan Janairun 2026.