1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Amurka ta kakaba wa gwamnatin Sudan takunkumai

June 28, 2025

Hukumomin Amurka sun sanar da kakaba wa gwamnatin Sudan takunkumai saboda zarginta da yin amfani da makamai masu guba a yakin da take gwabzawa da dakarun sa kai na RSF.

Abdel Fattah al-Burhan shugaban mulkin sojin Sudan
Abdel Fattah al-Burhan shugaban mulkin sojin SudanHoto: Sudan Transitional Sovereignty Council/Handout via REUTERS

A cikin wata sanarwa da ta wallafa a jiya Juma'a, ma'aikatar harkokin wajen Amurka ta tabbatar da cewa takunkumin na tsawon akalla shakara guda da aka labtawa Sudan din ya jibanci katse taimakon agajin gaggawa da kuma kayayyakin amfani gona.

Karin bayani: Gargadin yuwuwar kisan kare dangi a rikicin Sudan

A cewar Washington ta dauki wannan mataki ne saboda gwamnatin ta Sudan ta karya yarjejeniyar haramta yin amfani da makamai masu guba wadda aka amince da ita a watan Mayu na shekarar 1999.

A cikin watan Mayu da ya gabata ne dai Amurka ta zargi  Sudan da yin amfani da harantattun makamai masu guba a cikin shekarar 2024, zargin fadar mulki ta Khartoum ta musanta saboda rashin gabatar da gamsassun hujjoji.