1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sakon taya murnar Amurka ga Tinubu

March 2, 2023

Gwanmatin Amurka ta aike da sakon taya murnar nasarar Bola Ahmed Tinubu a matsayin zababben shugaban Najeriya.

Joe Biden
Joe BidenHoto: Susan Walsh/AP/picture alliance

A waje guda kuma fadar White House ta yi kira ga 'yan Najeriya da su kwantar da hankula bayan zarge-zargen magudi da matsaloli da aka fuskanta yayin zaben.

Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya bayyana sakon taya murnar ne a lokacin da yake ganawa da takwaransa na Najeriya Geoffrey Onyeama a wajen taron kasashe masu ci gaban masana'antu na G20 da ake yi a birnin New Delhi na kasar Indiya.

A cikin wata sanarwa, ma'aikatar harkokin wajen Amurka ta ce tana sane da korafin 'yan Najeriya da wasu jam'iyyun siyasar kasar suka bayyana kan damuwarsu game da zaben.

A waje guda kuma zababben shugaban na Najeriya Bola Ahmed Tinubu wanda ya yi alkawarin hada kan 'yan kasar ya yi kira ga jam'iyyun adawa da su manta da banbance-banbancen dake tsakaninsu su hada hannu don ciyar da kasar gaba.