An ɗage dokar ta ɓaci a kasar Philippines
March 3, 2006Talla
Shugabar ƙasar Philippines Gloria Arroyo ta ɗage dokar ta bacin na tsawon mako guda da aka sanya a ƙasar bayan yunƙurin juyin mulki da aka zargi wasu jamián sojin ƙasar da aikatawa. Shugabar kasar Gloria Arroyo ta sanar da dage dokar ta bacin ne a jawabin da ta yiwa alúmar ƙasar bayan da masu bata shawarar a kann alámuran tsaro suka tabbatar mata da cewa komai ya lafa, babu wata fargaba ta juyin mulkin a yanzu. A halin da ake ciki, an tuhumi a kalla mutane 50 waɗanda suka haɗa da yan adawa da kuma jamián soji da yunƙurin kifar da gwamnatin