SiyasaGabas ta Tsakiya
Iran ta aiwatar da hukuncin kisa kan dan jarida
December 12, 2020![Iran Journalist Ruhollah Zam](https://static.dw.com/image/55914443_800.webp)
Talla
Tun da farko dai mahukumtan na Iran sun kama shi da laifin zama kanwa-uwar-gami a zanga-zangar da aka yi wa gwamnati a shekara ta 2017.
Bayan da dan jaridar ya yi ta kauce-kauce domin tsira da rayuwarsa hukumomi sun kama shi har ma a shekarar da ta gabata kotun kolin kasar ta amince da aiwatar da hukuncin kisa a matsayin ladabtarwa ga laifin da suke ganin ya aikata wa kasar. Jaridar Amadnews ta dan jaridar dai nada mabiya fiye da miliyan daya a shafukan sada zumunta.