1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An amince da kwamitin yi wa kundin mulkin Masar kwaskwarima

February 6, 2011

A karon farko cikin lokaci mai tsawo gwamnatin Masar ta fara tattaunawa da 'yan adawa domin samun mafita daga dambarwar siyasar ƙasar.

Ganawa tsakanin gwamnatin Masar da shugabannin 'yan adawaHoto: dapd

Sakamakon matsin lamba daga zanga-zangar da aka shafe kusan makonni biyu ana yi a Masar, gwamnatin ƙasar ƙarƙashin shugaba Hosni Mubarak a karon farko ta fara tattaunawa da 'yan adawa. A wannan Lahadi dai a birnin Alƙahira, mataimakin shugaban ƙasa Omar Suleiman ya gana da wakilan ƙungiyar 'yan'uwa Musulmi wadda a hukumance an haramta ayyukanta da kuma sauran 'yan siyasa na ɓangaren adawa, inda suka tattauna game da makomar ƙasar. Wani kakakin gwamnati ya rawaito cewa a gun taron an amince da kafa wani kwamiti a cikin wata guda, wanda zai duba irin gyare gyaren da za a yi wa kundin tsarin mulkin ƙasar. To sai dai duk da haka har yanzu ana ci-gaba da zanga-zanga a tsakiyar birnin Alƙahira da ma wasu birane inda ake kira ga shugaba Mubarak da ya sauka daga kan karagar mulki.

A kuma halin da ake ciki a karon farko cikin mako guda an buɗe bankuna a faɗin ƙasar baki ɗaya.

Mawallafi: Mohammad Nasiru Awal
Edita: Umaru Aliyu