1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Za a gudanar da babban zabe a Libya

Abdul-raheem Hassan
June 18, 2026

Jiga-jigan da ke ja in ja a gwamnatin Libya sun cimma matsaya kan gudanar da zabe don kawo karshen rikicin siyasa da ya dade yana addabar ci gaban kasar.

Mata suna shewa da tutar Libya a birnin Tripoli a shekarar 2020
Mata suna shewa da tutar Libya a birnin Tripoli a shekarar 2020Hoto: Mahmud Turkia/AFP

Sanarwar ta hadin guiwa ta zo ne sa'o'i kadan kafin shugabar tawagar Majalisar Dinkin Duniya a Libiya Hanna Tetteh ta gabatar da jawabi ga kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya kan ci gaban da kasar ta samu a baya-bayan nan.

Shugabannin manyan cibiyoyin gwamnatin kasar sun amince da ci gaba da shirye-shiryen zaben shugaban kasa da na majalisar dokoki, bayan tattaunawa da aka yi domin warware sabanin da ya hana gudanar da zabe tun a 2021.

Majiyoyi sun ce bangarorin sun kuma jaddada muhimmancin hadin kai da samar da yanayin tsaro, don tabbatar da sahihin zabe a watan Febrairun 2027.

Libya ta shafe shekaru tana fama da rarrabuwar kawuna da gwagwarmayar siyasa tun bayan hambarar da tsohon shugaban kasar, Muammar Gaddafi a shekarar 2011. Ana fatan sabon yarjejeniyar za ta taimaka wajen kafa gwamnatin da za ta samu amincewar dukkannin bangarorin da ke gaba da juna.

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW