Za a gudanar da babban zabe a Libya
June 18, 2026
Sanarwar ta hadin guiwa ta zo ne sa'o'i kadan kafin shugabar tawagar Majalisar Dinkin Duniya a Libiya Hanna Tetteh ta gabatar da jawabi ga kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya kan ci gaban da kasar ta samu a baya-bayan nan.
Shugabannin manyan cibiyoyin gwamnatin kasar sun amince da ci gaba da shirye-shiryen zaben shugaban kasa da na majalisar dokoki, bayan tattaunawa da aka yi domin warware sabanin da ya hana gudanar da zabe tun a 2021.
Majiyoyi sun ce bangarorin sun kuma jaddada muhimmancin hadin kai da samar da yanayin tsaro, don tabbatar da sahihin zabe a watan Febrairun 2027.
Libya ta shafe shekaru tana fama da rarrabuwar kawuna da gwagwarmayar siyasa tun bayan hambarar da tsohon shugaban kasar, Muammar Gaddafi a shekarar 2011. Ana fatan sabon yarjejeniyar za ta taimaka wajen kafa gwamnatin da za ta samu amincewar dukkannin bangarorin da ke gaba da juna.