1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Zaman makoki na kwanaki 3 a Nijar

Binta Aliyu Zurmi
October 3, 2023

Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta ayyana zaman makoki na kwanaki 3, bayan wani mumunan kisan da 'yan bindiga suka yi wa sojoji 29 a kan iyakar kasar da Mali.

Niger | General Abdourahmane Tiani
Hoto: Balima Boureima/Reuters

Sanarwar ma'aikatar tsaron kasar na cewar 'yan bindiga sama da 100 sun yi amfani da motoci da ke shage da bama-bamai wajen illata sojoji. 

Sai dai ta yi ikirarin  murkushe barazanar da 'yan ta'addan ke yi a wannan yankin da ya jima yana fama da hare-hare.

Harin da ke zama mafi muni ga sojojin tun bayan da suka hambarar da gwamnatin farar hula a watan Yulin da ya gabata, na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin mulkin sojan kasar ta amince da tayin shiga tsakani daga Aljeriya domin warware rikicin siyasa. 

Tun a shekarar 2021 ne iyakokin kasashen Nijar da Mali da Burkina faso ke fama da ayyuukan yan ta'adda da ke da alaka da kungiyoyin al-Qaida da kuma na IS.