1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An fara bincike kan Mursi

July 13, 2013

An fara gudanar da bincike kan jerin korafe-korafen da wasu 'yan Masar ke da su kan hambararren shugaban kasar Muhammad Mursi da wasu jiga-jigan jam'iyyarsa.

Hoto: AP

Ofishin babban mai bincike na gwamnatin Masar din ne ya tabbatar da wannan labarin a wannan Asabar din (13. 07. 13), inda ya ce daga cikin abubuwan da su ke binciken sun hada da korafi na leken asiri da kitsa kisan masu zanga-zangar lumana da tabarbarewar tattalin arzikin kasar lokacin da ya ke kan mulki.

To sai dai yayin da aka fara gudanar da wannan bincike, Amirka da tarayyar Jamus a wannan Juma'a (12. 07. 13) sun yi kiran da a saki Mursin daga inda soji ke tsare da shi tun bayan da suka yi masa juyin mulki.

Su kuwa magoya bayan Mursi din na ci gaba da yin zanga-zanga ce domin neman a saki hambararren shugaban da ma dai maida shi kan karagar mulki.

Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Saleh Umar Saleh