1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An gana tsakanin Thabo Mbeki da Angela Merkel a birnin Berlin

July 8, 2006
Shugaban ATK Thabo Mbeki ya yi maraba da gudummawar da Jamus ke bayarwa a kasar JDK musamman ma wajen girke sojojin rundunar Bundeswehr. Bayan ganawar da yayi da SGJ Angela Merkel a birnin Berlin shugaba Mbeki ya ce duk wani ci-gaba da za´a samu a Kongo da kuma a Sudan yana da muhimmanci wajen samar da zaman lafiya da kwanciyar da kuma daidaituwar al´amuran siyasa a nahiyar Afirka baki daya. Wasu batutuwan da taron tsakanin shugabannin biyu ya tabo kuma sun hada da halin da ake ciki a Sudan da taron kolin kungiyar G-8 da zai gudana a karshen makon mai zuwa a birnin St. Petersburg na Rasha sai kuma batun shirin nukiliyar Iran da ake takaddama a kai. Merkel ta ce dukkan sassan zasu samu fa´ida idan Iran ta yarda da tayin taimako da KTT ta yi mata da nufin warware rikicin nukiliyar kasar.
Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW