1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An gaza sasanta Isra'ila da Hamas a Qatar

July 7, 2025

Zagaye na farko na tattaunawar tsagaita wuta tsakanin Isra’ila da kungiyar Hamas ya kare ba tare da cimma matsaya ba a birnin Doha na kasar Qatar, kamar yadda wasu majiyoyi daga Falasdinawa suka sanar a wannan Litinin.

Hoto: Saeed Jaras/Anadolu/picture alliance

Majiyoyin sun shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa bayan zaman farko na tattaunawar kai tsaye ta hanyar wakilai a Doha, wakilan Isra'ila sun nuna cewa ba su da cikakken izini ko iko da zai ba su damar kulla yarjejeniya da Hamas.

Kafar yada labaran BBC ta ruwaito cewa tattaunawar ta gudana ne a cikin gine-gine biyu dabam-dabam, kuma ta dauki kimanin sa'o'i uku da rabi.

An gudanar da tattaunawar ne ta hanyar masu shiga tsakani dagaQatar da Masar, amma ba a kai ga samar da wani ci-gaba ba. Amma ana sa ran za a ci gaba da tattaunawar nan ba da jimawa ba.