1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jami'an tsaro sun mutu a Nijar

Abdoulaye Mamane Amadou
June 11, 2021

Wani harin 'yan bindiga a Jamhuriyar Nijar ya hallaka jami'an tsaron kasar hudu a yayin da suke sintiri a saharar garin Assamaka da ke kan iyakar kasar da Aljeriya.

Niger Polizei in Niamey
Hoto: Getty Images/AFP/I. Sanogo

'Yan sanda uku da wani genderme guda ne suka game da ajalinsu, biyo bayan harin 'yan bindigar da ya auku lokacin da suke sintiri a yankin saharar da ke tsakanin kasashen Nijar da Aljeriya.

Ma'aikatar cikin gidan kasar da ta tabbatar da harin a cikin wata sanarwa, ta kuma bayyana a yammacin jiya da cewa, jami'anta sun yi nasarar fatattakar maharan tare lalata motocinsu, jim kadan bayan kai farmakin na Assamaka da ke Arewa maso yammacin kasar.

Ko a shekarar 2017 ma dai, rahotanni sun ce jami'an Nijar biyar ne a jimmalace suka mutu a yankin mai iyaka da Aljeriya, yankin da ta nan ne Aljeriyar ke dawo da dubban 'yan ci-rani da bakin haure da ke shigewa ta kasar ba tare da ka'ida ba.

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW