'Yan bindiga sun hallaka shugaban kasar Hait
July 7, 2021![Haiti Präsident Jovenel Moise](https://static.dw.com/image/58188067_800.webp)
Da yake tabbatar da aukuwar lamarin Mininstan cikin gidan kasar Claude Joseph ya ce maharan sun kai harin ne gidan shugaban kasar mai shekaru 53 da misalin karfe 1 na daren Talata kuma mai dakin shugaban kasar ta ji mummunar rauni inda take kwance a asibiti.
Harin dai na zuwa ne a daidai lokacin da rikicin siyasa ya dabaibaye kasar dake jerin kasashen Caribbean. Kuma ayyukan agaji ke fuskantar barazana yayin da ake fama da karancin abinci a kasar. Wutar rikicin ya kara ruruwa ne bayan da talauci ke neman yiwa kasar katutu wanda ya haifar da gudanar da jerin zanga-zanga tun bayan da marigayi Moise ya hau karagar mulki a shekarar 2017. A wannan shekarar ce dai 'yan adawa a kasar suka zargi shugaban da mulkin kama karya, zargin da ya musanta.