1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An ji amon harbe-harbe a Khartoum

Binta Aliyu Zurmi
April 26, 2023

An shiga rana ta biyu a yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma tsakanin Sojojin gwamnati da dakarun sa kai na rundunar RSF a kasar Sudan.

Sudan | Kämpfe in Khartoum
Hoto: AFP/Getty Images

To sai dai an ji amon harbe-harbe da shawagin jiragen yaki gami da tashin bama-bamai a birnin Khartoum a cewar jakada na musamman na Majalisar Dinkin Duniya a Sudan Volker Perthes, a yayin wata gamnawa da ya yi da kwamitin tsaro na Majalisar.

Perthes ya bayyana cewar yana ci gaba da tattaunawa da bangarorin sojojin da ke fada da juna, a cewarsa babu wata alama da ke nuna suna da muradin hawa teburin tattaunawa.

Hukumar Lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya, WHO ta yi gragadi a kan amfani da muggan sinadarai masu guba bayan da sojojin da ke fada da juna suka mamaye dakunan gwaje-gwajen kimiyya.

Ya zuwa yanzu, wannan rikici ya halaka rayukan mutane sama da 450 yayin da ya jikkata wasu dubbai.
 

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW