SiyasaAfirka
An ji karar harbi a kusa da fadar shugaban Guinea Conakry
February 10, 2026
Talla
Karar harbe-harben bindiga ta karade kewayen babban gidan yarin kasar Guinea da ke yankin Kaloum na Conakry, babban birnin kasar, wanda kuma ke kusa da fadar shugaban kasa, kamar yadda shaidu suka tabbatar.
Wasu da ke makwabtaka da kurkukun sun shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa AFP cewa sun fara jin harbe-harben ne da karfe 9 na safiyar Talata, daga nan aka ci gaba da luguden wutar harsasai har tsawon sa'a guda.
Karin bayani : Kotu ta tabbatar da nasarar Doumbuya
Tuni motocin silke na 'yan sanda da jami'an tsaro na musamman suka kafa shinge a kan hanyar zuwa kurkukun, kuma zuwa wannan lokaci babu wani karin bayanin abin da ke faruwa daga mahukuntan kasar.