1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

An ji tashin bama-bamai a birnin Yamai na Nijar

January 29, 2026

Kamfanin dillancin labarai na AFP ya tabbatar da cewa an ji karar harbe-harben bindigogi da ababan fashewa a kusa da filin jiragen sama na Diori Hamani da ke Yamai babban birnin kasar.

Sojojin Nijar da ke tsaron lafiyar Janar Abdourahamane Tiani a birnin Yamai
Sojojin Nijar da ke tsaron lafiyar Janar Abdourahamane Tiani a birnin YamaiHoto: Boureima Hama/AFP/Getty Images

Mazauna birnin sun shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa hayaki da haske ya turnuke sararin samaniyar birnin. Kazalika, wasu hotunan bidiyo da mazauna birnin suka wallafa a kafafen sadarwar intanet ya nuna yadda motocin sulke na sojoji ke sintiri a yankin.

Karin bayani:Nijar: Shekara guda bayan juyin mulkin soji

To amma rahotannin baya bayannan sun tabbatar da cewa al'amura sun lafa, kimanin awanni biyu da jin karar harbe-harben. Wani 'dan Nijar da ke goyon bayan gwamnatin soji, Ibrahim Bana, ya wallafa wani sako a shafinsa na Facebook, inda ya bukaci daukacin al'ummar kasar da su fito kwansu da kwarkwatarsu domin kare kasar daga duk wata barazana.

Karin bayani:Makomar Dimukuradiyya a kasashen da sojoji ke mulki

Babu rahotannin asarar rayuka sakamakon farmakin na birnin Yamai, da ke zama barazana ga gwamnatin Janar Abdourahamane Tiani, wanda ya hau kan karagar mulki shekaru biyu da suka gabata bayan hambarar da gwamnatin dimukuradiyya.