Sabuwar gwamnatin hadin kan kasa a Libya
January 19, 2016Talla
Tun dai a kwanakin baya ne majalisar dinkin duniya ta bukaci ‘yan majalisar kasar dasu amince da kafa sabuwar gwamnatin, wacce kuma Fayez al-Sarraj hamshakin attajiri nan ya ke ma jagoranci.
Kazalika a nasa bangaren ministan harkokin wajen Libyan Mohammed Al-Dairi cewa yake.
kafa gwamnatin hadin kan kasar libyan yana da matikar mahimanci musamman ga al'umomin kasa da kasa a dai-dai lokacin da suka yi mana nuni da cewar sai mun yi hakan za a janye mana takunkumi da suka hada da makamai ta yadda za mu cigaba da yakar ta'addanci.
Tun dai a shekara ta 2011 kasar Libyan ta tsunduma cikin rikita- rikitar siyasa tare da zubar da jini tsakanin bangarori biyu da basa ga muciji da juna sakamakon hambarar da Mamman Gadafi a gadon mulkin kasar.