1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Hari a Jamhuriyar Benin

Suleiman Babayo AH
June 6, 2025

Mayakan jihadi sun halaka jami'an tsaron Jamhuriyar Benin, inda lamuran tsaro ke kara tabarbarewa a kasar da ke yankin yammacin Afirka.

Jamhuriyar Benin
Jamhuriyar BeninHoto: Marco Simoncelli/DW

Rahotanni da kasar Jamhuriyar Benin sun nuna cewa wani harin mayakan masu ikirarin jihadi ya halaka sojoji uku da 'yan sanda biyu a yankin arewa masu yammacin kasar. Majiyoyin tsaro sun ce an kai hari a ofishin 'yan sanda na Tanougou.

Karin Bayani: Mayakan jihadi sun kashe sojojin Benin 70

Ita dai Jamhuriyar Benin tana fuskantar tashe-tashen hankula na kungiyoyin Jihadi a iyakar kasarda kasashen Burkina Faso da kuma Jamhuriyar Nijar.

Kasashe uku na Mali da Burkina Faso gami da Jamhuriyar Nijar suna fuskantar hare-hare tsageru masu ikirin jihadi, inda sojoji suka yi juyin mulki a duk kasashen uku, sannan kasashen uku suka fice daga kungiyar bunkasa tattalin arzikin kasashen Afirka ta Yamma ECOWAS.