An kai hari kan sojojin Yemen
December 29, 2019![Jemen Anschlag auf Polizeikräfte in Aden](https://static.dw.com/image/49839710_800.webp)
Talla
Wasu hotunan harin da ke yawo a yanar gizo ya nuna gawarwakin mutane da dama a kwance, sama da mutane 20 sun jikkata.
Dakarun kasar Yemen na zargin mayakan Houthi da kai harin, sai dai 'yan tawayen ba su ce komai ba.
An fara yakin kasar Yemen a 2014 bayan da 'yan Houthi suka nuna sha'awar kwace iko da babban birnin aksar Sana'a, suka tilastawa Shugaba Abed Rabbo
Mansour Hadi yin hijira.