1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kai mummunan hari cocin Koptik a Masar

April 9, 2017

Tagwayen hare haren wadanda aka kai Cocin mabiya darikar Koptik ya hallaka mutane akalla 40 tare da jikata wasu da dama.

Ägypten nach Anschlag auf Kirche inTanta
Hoto: Reuters/M. Abd el Ghany

A kasar Masar wasu tagwayen hare-haren ta'addanci da aka kai a wasu Coci-Coci a birane biyu na kasar a wannan Lahadi sun yi sanadiyyar mutuwar mutane kimanin 40. Gwamnatin kasar ta tabbatar da cewa hari na farko an kai shi ne da misalin karfe goma na safiyar yau a Cocin Kiristoci mabiya darika Koptika na garin Tanta da ke a nisan kilomita 120 arewacin birnin Alkahira inda mutane akalla 25 suka rasu a yayin da wasu 78 suka ji rauni 

Tashar talabijin ta Etra News mai zaman kanta a kasar ta Masar ta nuna cikin ginin Cocin da irin yadda jini ya fantsama ko ina a saman ginin dama yadda kujerun zama na cikin cocin suka kaca kaca

Hari na biyu wanda na kunar bakin wake ne an kai shi ne a Cocin birnin Alexandrie, inda ya zuwa yanzu aka tabbatar da mutuwar mutane 11 a yayin da wasu 35 suka sami raunuka. Tuni dai Kungiyar IS ta dauki alhakin kai wadannan hare-hare na wannan rana ta lahadi a kasar ta Masar.