1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Harin kan fararen hula a Burkina Faso

Abdourahamane Hassane
May 19, 2023

An kashe fararen hula guda 20 da suka hada da mata da kananan yara a yayin wasu hare-hare biyu da ake zargin mayakan jihadi suka kai a tsakiyar gabashin Burkina Faso a cewar majiyoyin tsaro.

Burkina Faso Trauer Tote Anschlag
Hoto: Vincent Bado/REUTERS

Kungiyoyi masu dauke da makamai sun kai farmaki cikin garin Bilguimdure, wani kauye da ke cikin gundumar Sangha, a lardin Kulpélogo da ke a tsakiyya maso gabashin Burkina Fason mai iyaka da kasashen Ghana da Togo, inda suka kashe mutane goma. Kasar Burkina Faso, wacce ta fuskanci juyin mulki har sau biyu a shekarar ta 2022, ta fada cikin tashin hankali na masu jihadi a shekara ta 2015. wanda ya yi sanadin mutuwar mutane fararen hula da sojoji fiye da dubu goma.

 

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW