1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Burkina Faso: Harin ta'addanci ya rutsa da farar hula

Abdourahamane Hassane
August 5, 2021

Masu Jihadi a Burkina Faso sun kashe goman mutane a kauyuka da da ke a arewacin kasar cikin Sahel

Burkina Faso Symbolbild Anschlag
Hoto: Issouf Sanogo/AFP

Majiyoyin tsaro sun ce an samu gawarwaki mutane da yawa a cikin kauyuka wadanda masu jihadi suka yi wa yanka rako. Yan ta'addar sun kai hare-haren nea kauyukan Banogo da Basian da Tokabangou da Gadba da kuma Pensa da ke kan iyaka da Nijar, majiyoyin  sun ce a harin masu jihadin sun kashe 'yan kato da gora da dama wadanda ke tallfa wa sojoji a cikin aikin kula da tsaro.