1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kashe masu zanga-zanga a Masar

Carl Richard HolmMarch 29, 2014

Mutane aƙalla guda biyar aka kashe a birnin Alƙahira a lokacin wani yamutsin da magoya bayan Ƙungiyar 'Yan Uwa Musulmi suka gudanar.

Kairo Zusammenstöße
Hoto: Reuters

Ofishin ministan cikin gida na ƙasar Masar ya ce aƘalla mutane guda biyar aka kashe a birnin alƙahira a sakamakon arangamar da aka sha tsakanin magoya bayan Ƙungiyar 'Yan Ua Musulmi da ke yin zanga-zangar da kuma jami'an tsaro.

Masu aiko da rahotannin sun ce a cikin waɗanda aka kashen har'da wata 'yar jarida Mayada Ashraf ta jaridar Alnusura wacce ta gamu da ajalinta a fagen daga a lokacin da take yin aikin ɗaukar rahotanni a kan zanga-zangar. Magoya bayan hamɓararran shugaban ƙasar wato Mohammed Mursi sun gudanar da zanga-zangar ne, domin nuna adawa da hukuncin kisan da aka yankewa wasu magoya bayan ƙungiyar kusan ɗari biyar. Gwamnatin dai ta ce ta kama mutane 73 a duk faɗin ƙasar waɗanda take zargi da yin amfanin da makamai a wajen zanga-zangar.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Mouhamadou Awal Balarabe