1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An Kashe mayakan IS a Masar

July 9, 2017

'Yan sanda a Masar, sun kashe wasu da ake ganin 'yan bindigan IS ne su 14, a wani farmaki da suka kai har tungarsu 'yan jihadin a gabashin lardin Islamiyya.

IS Kämpfer Videostill
Hoto: picture-alliance/AP Photo

Mahukunta a Masar, sun ce sun halaka 'yan bindigan IS din ne su 14, a farmaki da suka kai har maboyar 'yan jihadin a gabashin lardin Islamiyya. Sanarwar masu kayan sarkin na zuwa ne kasa da sa'o'i 48 da IS ta kaddamar wani hari a kan sojin kasar.

A cewar ministan harkokin cikin gidan kasar ta Masar, 'yan sandan sun afka wa mayakan na IS ne a gabashin lardin Islamiyya yankin da IS din ke da sansani a can. Gwamnatin Masar ta kuma ce biyar daga cikin 'yan bindigan, na cikin jerin wadanda da ma take nema 'ruwa a jallo'.

Ko a Juma'ar da ta gabata ma dai mayakan na tarzoma sun kaddamar da hare-hare a wasu shingayen bincike da ke yankin Sinai, inda suka yi ruwan Bama-Bamai gami da albrusai, sai dai jami'ai sun yi ikirarin kashe su da dama.

 

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW