1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kashe mutane a wata masha a Kamaru

Abdul-raheem Hassan
September 15, 2026

Rahotanni daga Arewa maso yammacin Kamaru na cewa 'yan bindiga sun kashe mutane uku tare da jikkata wasu hudu bayan da suka bude wuta a wata mashaya a binrin Bamenda.

Jami'in kwantar da tarzoma na MDD a tsaye a kan iyakar Kamaru
Jami'in kwantar da tarzoma na MDD a tsaye a kan iyakar KamaruHoto: Camille Laffont/AFP/Getty Images

Hukumomi sun ce harin ya faru ne da yammacin Litinin, amma ba su bayyana wadanda suka kai harin ba zuwa yanzu. Yankunan da ake magana da Ingilishi a Kamaru sun shafe kusan shekaru goma suna fama da rikici tsakanin jami'an gwamnati da kungiyoyin masu neman ballewa wato Ambazoniya.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce akalla mutane 6,000 sun mutu tun bayan barkewar rikicin, yayin da daruruwan dubban mutane suka rasa matsugunansu a Kamaru. A shekarar 2025, sama da mutane 100,000 sun tsere daga kasar zuwa Najeriya saboda rikicin.