An kashe wasu sojojin Najeriya
December 16, 2018Rahotannin da ke fitowa daga Najeriya, na cewa akalla sojojin kasar biyu ne suka mutu sakamakon tashin wata nakiya a gefen hanya, kamar dai yadda wata majiya ta tsaro ta tabbatar.
Sojojin na aikin sintiri ne cikin jerin gwanon motoci a garin Gamboru na jihar Borno a shiyar arewa maso gabashin kasar, garin da ke iyakan Najeriyar da Kamaru.
Yankin dai, yanki ne da 'yan kungiyar Boko Haram bangaren Abubakar Shekau ke da karfi a ciki, kuma an saba yi wa sojojin irin wannan takon lokacin da suke sintiri.
A share guda kuwa daya bangaren kungiyar mai alaka da kungiyar IS, ya kai wani harin da yammacin Juma'ar da ta gabata a sansanin soji da ke Gudumbali cikin gundumar Guzamala, sai dai sojojin sun murkushe mayakan ba tare da labarin rasa wani jami'i ba.